Ƴan bindiga sun sako kwamishina da suka sace a jihar Nasarawa

Yakubu Lawal, kwamishinan yada labarai, al’adu da yawon bude ido na jihar Nasarawa wanda yan bindiga suka yi garkuwa da shi ya shaki iskar yanci.

Ramhan Nansel, mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Nasarawa, shi ne ya sanarwa da kamfamin dillancin labarai na Najeriya NAN haka ranar Juma’a.

Kwamishinan an yi garkuwa da shi a ranar Litinin a gidansa dake Nasarawa Eggon.

Nansel ya ce kwamishinan ya shaki iskar yanci da misalin karfe 06:00 na yammacin ranar Juma’a kuma tuni ya isa gida wurin iyalinsa.

Mai magana da yawun rundinar ya ce babu wani da aka kama da zargin sace shi.

More News

Atiku ya bayar da tallafin miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri babban birnin...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

Mutanen Sokoto na ta murnar kashe ƙasurgumin ɗanbindigar nan Halilu Buzu

Mazauna yankin Sokoto da kewaye na murnar kashe wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Kachallah Halilu Buzu, da sojojin Najeriya suka yi a farmakin da...