Dan Majalisar Jihar Kaduna, Hon. Usman Garba Zingo, ya shaki iskar ’yanci bayan da ’yan bindiga suka sake shi a yammacin ranar Lahadi, lamarin da ya sanya iyalansa, magoya bayansa da al’ummar yankinsa cikin farin ciki.
Rahotanni sun ce an sace shi ne yayin da yake kan hanyarsa daga Jihar Zamfara zuwa Kaduna. Sai dai Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta musanta cewa an yi garkuwa da shi.
Wani masani kan harkokin tsaro a Arewa maso Yamma, Bakatsine, ya wallafa wani bidiyo a shafinsa na X inda aka ga jama’a na taya dan majalisar murnar dawowarsa lafiya.
Har yanzu ba a bayyana yadda aka samu sakinsa ba, ko an biya wani sharadi, domin babu wata sanarwa a hukumance daga jami’an tsaro ko iyalansa kan yadda aka kubutar da shi.
Bayan yaduwar labarin dawowarsa, mazauna yankinsa sun taru domin tarbarsa, suna godiya ga Allah Madaukakin Sarki bisa dawowarsa lafiya. Har zuwa yanzu dai babu wata sanarwa a hukumance da aka fitar dangane da sakinsa.
Ƴan Bindiga Sun Saki Dan Majalisar Kaduna, Usman Garba Zingo

