Ƴan bindiga sun kashe ɗan sanda da wasu mutane uku a Abia

Ƴan bindiga sun kashe Shehu Oyibo wani insifectan ƴan sanda da wasu mutane uku a jihar Abia.

An yi kisan ne a ranar Lahadi akan titin Ngwa dake garin Aba  yayin wata musayar wuta tsakanin maharan da kuma jami’an ƴan sandan da suke gudanar da sintiri.

Maureen Chinaka, mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Abia ta ce biyu daga cikin ƴan bindigar sun mutu a yayin musayar wuta.

Chika Godliveth, Onyenaturuchi Jonah, a Eniobong Godsgift Clement su ne sauran mutanen da aka kashe a harin.

Chinaka ta ce an ajiye gawar mutanen a ɗakin ajiye gawarwaki.

Ta tabbatarwa da al’umma cewa rundunar za ta cigaba da tsaron rayukansu kuma tuni aka fara gudanar da bincike kan harin.

Jihar ta Abia na ɗaya daga cikin jihohin yankin kudu maso gabas da suke fuskantar matsalolin tsaro sakamakon ayyukan mayaƙan ƙungiyar IPOB dake fafutukar neman kafa ƙasar Biafara.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...