Ƴan bindiga sun kai hari gidan kwamishinan zaɓe na jihar Kogi

Wasu yan bindiga sun kai hari gidan kwamishinan zaɓe na jihar Kogi dake Lokoja da tsakar daren ranar Alhamis.

A cikin wata sanarwa da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa, INEC ta fitar ta ce maharan sun kai harin ne da misalin ƙarfe 03:30 na dare.

Sanarwar ta ce maharan sun shafe sama da minti 30 suna musayar wuta da jami’an tsaro kafin ƙarin wasu jami’an tsaro su kawo musu ɗauki.

Babu ko da mutum guda da ya rasa ransa a harin sai dai an tafka asarar dukiya ta miliyoyin naira.

Harin na ranar Alhamis na zuwa ne ƴan kwanaki bayan wasu ƴan bindiga suka kai hari ofishin hukumar zabe ta INEC dake jihar.

More News

Gwamnatin Abia za ta fara biyan albashi mafi maranci na naira 70,000 a watan Oktoba

Gwamnatin Jihar Abia ta sanar da cewa za ta fara biyan sabon albashi mafi karanci na naira 70,000 ga ma’aikatanta daga watan Oktoba 2024.Kwamishinan...

Sojoji sun lalata haramtattun matatun mai 32 a yankin Neja Delta

Dakarun sojan Najeriya na runduna ta 6 dake Fatakwal sun samu nasarar lalata haramtattun matatun man fetur 32 tare da ƙwace lita 250,000 na...

An gudanar da bikin cikar Kwankwaso shekara 68.

Tarin magoya baya da kuma abokanan siyasar tsohon gwamnan jihar Kano, Sanata Rabi'u Kwankwaso ne suka halarci taron lakca da aka shirya domin bikin...

Faruk Lawan ya kammala zaman gidan yarin Kuje

An sako tsohon ɗan majalisar wakilai ta tarayya, Hon Faruk Lawan daga gidan yarin Kuje bayan da ya kammala zaman gidan yarin na shekaru...