Ƙungiyar NLC za ta yi taro don tattauna wahalhalun da ƴan Najeriya ke sha saboda tsadar fetur

Mataimakin sakataren kungiyar ƙwadago ga NLC na kasa, Chris Onyeka, ya ce kwamitin gudanarwa na kungiyar zai yi wani muhimmin taro a yau tare da daukar matsaya kan tsadar man fetur a Najeriya.

Ya ce duk wasu batutuwan da suka shafi wahalhalun da talakawa ke ciki saboda tashin farashin mai na baya-bayan nan, za a duba su a wurin taron.

“Za mu bai wa Gwamnatin Tarayya wa’adi. Mun ba su isasshen abin da za su kula da ’yan Najeriya su gyara, amma sun ki gyara. Su shirya kansu domin muna shiri. A shirye muke mu yaƙe su,” inji shi.

A halin da ake ciki kuma, kungiyar Kwadago ta yi watsi da shirin bai wa gwamnatocin jihohi damar fitar da kayan agaji ga ‘yan kasa domin rage wahalhalun da suke fuskanta sakamakon cire tallafin man fetur.

Idan ba a manta ba, Shugaban kasa Bola Tinubu a jawabinsa na kaddamarwa a ranar 29 ga watan Mayu ya sanar da kawo karshen tsarin tallafin man fetur wanda nan take ya rufe farashin famfon na Premium Motor Spirit wanda aka fi sani da man fetur daga Naira 165 kan kowace lita zuwa N540.

A halin yanzu ana sayar da man tsakanin N568 zuwa N617 kowace lita.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waɗanda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...