Ɗan ta’addar Boko Haram ya miƙa kansa ga sojoji

Alhaji Wosai wani mamba a ƙungiyar ƴan ta’addar Boko Haram ya miƙa kansa ga dakarun sojan Najeriya na rundunar Operation Haɗin Kai.

Rahotanni sun bayyana cewa ɗan ta’addar ya miƙa kansa ga dakarun 21 Amored Brigade bayan da ya gudo daga sansanin mayaƙan na ƙungiyar Boko Haram dake ƙauyen Garno a jihar Borno.

Wasu majiyoyin jami’an tsaron sirri sun faɗawa Zagazola Makama dake wallafa bayanai kan sha’anin tsaro a yankin tafkin Chadi cewa ɗan ta’addar ya miƙawa sojoji bindiga ƙirar AK-47 guda ɗaya gidan zuba harsashi guda ɗaya dake ɗauke da harsashi 39.

Ana cigaba da samun ƴan ta’addar Boko Haram dake miƙa kansu ga jami’an tsaro biyo baya matsin lamba ta hanyar farmaki da dakarun sojan Najeriya suke cigaba da yi musu.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...