Ɗalibin jami’a ya yi yunkurin kashe kansa kan sakamakon kammala karatu da aka riƙe masa tsawon shekaru 5

Wani ɗalibi da ya kammala Jami’ar Ambrose Ali(AAU) dake Ekpoma a jihar Edo ya yi yunkurin hallaka kansa bayan da ya zargi jami’ar da kin bashi takarardar sakamakon kammala karatu.

Ɗalibin mai suna Precious Ogbeide ya kammala karatu a Jami’ar a shekarar 2018 amma ya koka cewa ba a bashi takarardar kammala karatu ba.

Jaridar Punch ta rawaito cewa iyayen Ogbeide sun bayyana cewa ya dadde yana fama da matsananciyar damuwa saboda rashin karbar shedar kammala jami’ar bayan da ya shafe shekaru biyar yana karatu.

Ɗalibin ya rika kekketa jikinsa da guntun fasasshiyar kwalba.

Suma wasu tsofaffin daliban jami’ar sun koka kan yadda har yanzu jami’ar ta gaza basu shedar kammala karatu.

More News

An sake gano gawar wani shugaban Fulani da ya ɓata a jihar Filato

An gano gawar wani Arɗon Fulani, Umar Ibrahim da ya ɓace a cikin wata rijiya dake kauyen Jokom a ƙaramar hukumar Mangu ta...

An kama ƴan kungiyar IPOB 18 da ake zargi da kisan ƴan sanda

Rundunar yan sandan jihar Imo ta kama mutane 18 da ake zargi da zama yan kungiyar IPOB da suke da hannu a kisan ƴan...

Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da zaɓen gwamnan jihar Sokoto

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja ta tabbatar da zaɓen, Ahmed Aliyu a matsayin gwamnan jihar Sokoto. Rukunin alkalan kotun su uku sun yi watsi da...

Kotun ɗaukaka ta soke zaɓen shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja, ta soke zaɓen kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Liman. Alkalan kotun uku sun bayar da umarni da a sake...