Ƴansanda sun kama wanda ya kitsa harin da aka kai wa jirgin ƙasa a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Alhamis, ta sanar da kame wanda ake zargin ya shirya harin da aka kai a jirgin ƙasan Abuja-Kaduna inda aka kashe wasu fasinjoji.

An bayyana wanda ya shirya harin da suna Ibrahim Abdullahi, wanda kuma aka fi sani da Mandi.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar, ACP Olumuyiwa Adejobi, wanda ya bayyana hakan a Kaduna a ranar Alhamis, ya kuma bayyana cewa wanda ake zargin yana cikin waɗanda suka sace daliban jami’ar Greenfield a shekarar 2021.

Adejobi ya kuma kara da cewa an kama shi da bindigun AK-47 guda 48, kuma ana ci gaba da kokarin gano wanda ya dauki nauyinsa da kuma sama masa da makamai.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...