Ƴan sanda sun kama wasu sojan gona biyu

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta ce ta kama ta ce ta kama wasu sojan gona guda biyu Jonathan Yahaya da Muhammad Umar.

Benjamin Hundeyin mai magana da yawun rundunar shi ne ya bayyana haka a ranar Laraba.

Hundeyin ya ce wani soja mai muƙamin manjo ne dake barikin soja ta shiya ta 81 da ake kira Nigerian Army Provost, Bonny Camp, Victoria Island, Lagos shi ne ya kai mutanen biyu ofishin ƴan sanda na Onikan bayan da aka kama su.

Mai magana da yawun rundunar ya ce  sojoji sun kama ɗaya daga cikin mutanen ne sanye da wandon kakin soja da kuma takalmi a yayin da ɗayan kuma aka kama shi sanye da kakin soja.

“Biyo bayan tambayoyi an gano cewa dukkanin mutanen biyu sojan gona ne. Sun gaza faɗar yadda suka mallaki kakin soja  shine dalilin kama su.” a cewar Hundeyin.

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da ƴan ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an ƴan sanda da kuma sojoji suna ɗaukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar ƴan sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe ɗan Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...