Ƴan sanda sun kama wasu sojan gona biyu

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta ce ta kama ta ce ta kama wasu sojan gona guda biyu Jonathan Yahaya da Muhammad Umar.

Benjamin Hundeyin mai magana da yawun rundunar shi ne ya bayyana haka a ranar Laraba.

Hundeyin ya ce wani soja mai muƙamin manjo ne dake barikin soja ta shiya ta 81 da ake kira Nigerian Army Provost, Bonny Camp, Victoria Island, Lagos shi ne ya kai mutanen biyu ofishin ƴan sanda na Onikan bayan da aka kama su.

Mai magana da yawun rundunar ya ce  sojoji sun kama ɗaya daga cikin mutanen ne sanye da wandon kakin soja da kuma takalmi a yayin da ɗayan kuma aka kama shi sanye da kakin soja.

“Biyo bayan tambayoyi an gano cewa dukkanin mutanen biyu sojan gona ne. Sun gaza faɗar yadda suka mallaki kakin soja  shine dalilin kama su.” a cewar Hundeyin.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...