Ƴan sanda sun kama wani gawurtaccen mai garkuwa da mutane a Kaduna

Jami’an ƴan sanda sun samu nasarar kama wani gawurtaccen mai garkuwa da mutane a jihar Kaduna.

Mutumin da aka kama mai suna, Muhammad Bello ɗan shekara 30 na zaune ne a yankin  Yan Bokolo a Malalin Gabas dake ƙaramar hukumar Igabi ta jihar Kaduna.

Jami’an ƴan sandan rundunar Operation Yaƙi su ne suka kama shi a ranar 21 ga watan Mayu biyo bayan bayanan sirri da suka samu daga Sashen Bayanan Sirri na hedkwatar rundunar ƴan sanda dake Abuja.

Mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Kaduna, ASP Mansir Hassan cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a ya ce binciken farko da aka gudanar ya nuna cewa wanda aka kaman na da alaƙa da Dogo Haliru gawurtaccen mai garkuwa da mutane da aka sani da addabar jihohin Zamfara,Katsina da kuma babbar hanya hanyar Abuja zuwa Kaduna.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...