Ƴan sanda sun kama wani dillalin miyagun ƙwayoyi a jihar Lagos

Rundunar ƴan sandan jihar Lagos ta kama wani mai suna,Orji Isaac ɗan shekara 67 da aka samu da laifin sayar da miyagun kwayoyi a jihar.

Jami’an rundunar yan sandan jihar sun kama wanda ake zargin ne a yayin wani samame da suka kai yankin Yaba a ranar Laraba.

Benjamin Hundeyin mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ya ce an kama wani mai suna Lekan Ganiyu ɗan shekara 22 a lokacin da yake sayan ƙwayar a wurin mutumin da aka kama.

Za a gurfanar da mutanen biyu gaban kotu bayan kammala bincike.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...