Ƴan Majalisar Dokokin jihar Rivers 27 Sun Koma Jam’iyar APC

Yan majalisar dokokin jihar Rivers 27 ne cikin 32 suka sauya sheka daga jam’iyar PDP mai mulkin jihar ya zuwa jam’iyar adawa ta APC.

Ƴan majalisar sun sauya shekar ne a cikin wani hoto da suka ɗauka tare suna riƙe da tutar jam’iyar APC.

Sun bayyana cewa rabuwar kai da aka samu a cikin jam’iyar PDP shi ne babban dalilin su na sauya shekar.

Wannan cigaban da aka samu zai kara ruruta rikicin siyasar da ake fama da shi a jihar tsakanin tsohon gwamna, Nyesom Wike da kuma gwamna mai ci Siminalayi Fubara.

More from this stream

Recomended