Ƴan Majalisar Dokokin jihar Rivers 27 Sun Koma Jam’iyar APC

Yan majalisar dokokin jihar Rivers 27 ne cikin 32 suka sauya sheka daga jam’iyar PDP mai mulkin jihar ya zuwa jam’iyar adawa ta APC.

Ƴan majalisar sun sauya shekar ne a cikin wani hoto da suka ɗauka tare suna riƙe da tutar jam’iyar APC.

Sun bayyana cewa rabuwar kai da aka samu a cikin jam’iyar PDP shi ne babban dalilin su na sauya shekar.

Wannan cigaban da aka samu zai kara ruruta rikicin siyasar da ake fama da shi a jihar tsakanin tsohon gwamna, Nyesom Wike da kuma gwamna mai ci Siminalayi Fubara.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...