Ƴan Majalisar Dokokin jihar Rivers 27 Sun Koma Jam’iyar APC

Yan majalisar dokokin jihar Rivers 27 ne cikin 32 suka sauya sheka daga jam’iyar PDP mai mulkin jihar ya zuwa jam’iyar adawa ta APC.

Ƴan majalisar sun sauya shekar ne a cikin wani hoto da suka ɗauka tare suna riƙe da tutar jam’iyar APC.

Sun bayyana cewa rabuwar kai da aka samu a cikin jam’iyar PDP shi ne babban dalilin su na sauya shekar.

Wannan cigaban da aka samu zai kara ruruta rikicin siyasar da ake fama da shi a jihar tsakanin tsohon gwamna, Nyesom Wike da kuma gwamna mai ci Siminalayi Fubara.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...