Ƴan Fashin daji sun kashe sojoji 4 a Zamfara

Edward Buba daraktan yaɗa labarai na ma’aikatar tsaron Najeriya ya ce sojoji huɗu ƴan ta’adda suka kashe ranar Lahadi a wani harin kwanton ɓauna da aka kai musu.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, Buba ya ce sojojin sun fuskanci hare-haren kwanton ɓauna har sau biyu daga ƴan fashin daji a ƙauyen Kuran Mota da kuma a kan hanyar Alikere zuwa Yarmalimai dake jihar ta Zamfara.

Ɓuba ya ƙara da cewa sojoji uku sun jikkata a harin.

Ya ce sojojin sun samu nasarar kashe wasu daga cikin ƴan ta’addar biyo bayan da tallafin dakarun sojan sama da suka samu a lokacin fafatawar.

” A ranar 12 ga watan Mayu dakarun rundunar Operation Hadarin Daji sun fuskanci harin kwanton ɓauna sau biyu daban-daban ɗaya a ƙauyen Kuran Mota da kuma akan titin Alikere-Yarmalimai  a jihar Zamfara,” a cewar sanarwar.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...