Ƴan Fashin daji sun kashe sojoji 4 a Zamfara

Edward Buba daraktan yaɗa labarai na ma’aikatar tsaron Najeriya ya ce sojoji huɗu ƴan ta’adda suka kashe ranar Lahadi a wani harin kwanton ɓauna da aka kai musu.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, Buba ya ce sojojin sun fuskanci hare-haren kwanton ɓauna har sau biyu daga ƴan fashin daji a ƙauyen Kuran Mota da kuma a kan hanyar Alikere zuwa Yarmalimai dake jihar ta Zamfara.

Ɓuba ya ƙara da cewa sojoji uku sun jikkata a harin.

Ya ce sojojin sun samu nasarar kashe wasu daga cikin ƴan ta’addar biyo bayan da tallafin dakarun sojan sama da suka samu a lokacin fafatawar.

” A ranar 12 ga watan Mayu dakarun rundunar Operation Hadarin Daji sun fuskanci harin kwanton ɓauna sau biyu daban-daban ɗaya a ƙauyen Kuran Mota da kuma akan titin Alikere-Yarmalimai  a jihar Zamfara,” a cewar sanarwar.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...