Ƴan fashin daji sun kashe ɗan sanda ɗaya a wani shingen bincike a Zamfara

Ƴan fashin dajin a ranar Lahadi sun kai da farmaki kan wani shingen binciken ƴan sanda inda suka kashe ɗan sanda guda ɗaya tare da jikkata Wasu.

Shingen binciken an kafa shi ne tazarar  ƙasa da kilomita ɗaya kafin ka isa Kwatarkwashi garin dake kusa da Gusau babban birnin jihar.

Majiyoyi da dama sun faɗawa jaridar Daily Trust cewa ƴan fashin dake kan babura sama da 40 sun kai farmakin ne da misalin ƙarfe 04:00 na asubahin ranar Lahadi.

Ƴan fashin sun ƙona duk wani mai muhimmanci da suka samu a shingen binciken kafin su  bar wurin.

A cewar wata majiya ƴan fashin dajin sun samu nasarar fin ƙarfin ƴan sandan abun da yasa wasu daga cikinsu suka tsere bayan an ɗauki lokaci suna musayar wuta.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...