Ƴan bindiga sun sace wasu ɗalibai a jihar Delta

Rahotanni na cewa ƴan bindiga sun sace dalibai da kawo yanzu ba a san yawan adadinsu ba akan babbar hanyar east-west a ƙaramar hukumar Ughelli ta jihar Delta..

A cewar jaridar The Cable ɗaliban dake cikin mota ƙirar Sienna na kan hanyarsu ta dawowa daga birnin Calabar ne  na jihar Cross River lokacin da aka farma motar ta su da yammacin ranar Juma’a.

Mai magana da yawun rundunar ƴan sandan jihar Delta,Bright Edafe shi  ne ya tabbatarwa da jaridar faruwar haka a ranar Litinin.

Edafe ya ce jami’an ƴan sanda na bin sawun masu garkuwar domin kuɓutar da ɗaliban.

Lamarin ya shiga jerin ƙarin yawan ɗaliban da aka yi garkuwa da su a Najeriya.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...