Ƴan ƙwadago sun janye yajin aiki a Najeriya

Mambobin kungiyar kwadagon da suka hada da Nigeria Labour Congress da Trade Union Congress, a ranar Talata, sun dakatar da yajin aikin na kwanaki biyar, kamar yadda wani jigo a kungiyar NLC ya shaida a Abuja.

Ana sa ran kungiyoyin za su fitar da sanarwa jim kadan kafin a fara tattaunawa da gwamnati.

Yajin aikin wanda ya fara a ranar Litinin an yi shi  ne domin nuna rashin amincewa da gazawar gwamnatin tarayya na amincewa da sabon mafi karancin albashin a ranar 31 ga watan Mayu da kuma gazawarta wajen sauya karin kudin wutar lantarki.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...