Ƴan ƙwadago sun janye yajin aiki a Najeriya

Mambobin kungiyar kwadagon da suka hada da Nigeria Labour Congress da Trade Union Congress, a ranar Talata, sun dakatar da yajin aikin na kwanaki biyar, kamar yadda wani jigo a kungiyar NLC ya shaida a Abuja.

Ana sa ran kungiyoyin za su fitar da sanarwa jim kadan kafin a fara tattaunawa da gwamnati.

Yajin aikin wanda ya fara a ranar Litinin an yi shi  ne domin nuna rashin amincewa da gazawar gwamnatin tarayya na amincewa da sabon mafi karancin albashin a ranar 31 ga watan Mayu da kuma gazawarta wajen sauya karin kudin wutar lantarki.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...