Ƙungiyar ƙwadago ta ƙi amincewa da ₦48,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Taron zaman ganawa da ƴan kungiyar ƙwadago da gwamnatin ta tarayya ta kira  ya tashi babu shiri bayan da wakilan kungiyar ƙwadago suka fice daga taron.

Gwamnatin ta kira taron ne domin tattaunawa kan batun mafi ƙarancin albashi da za a riƙa biyan ma’aikata a Najeriya.

Joe Ajaero shugaban ƙungiyar ƙwadago ta NLC da kuma Tommy Okon mataimakin shugaban ƙungiyar ƙwadago ta TUC sune suka wakilci ma’aikata a wurin taron.

Da yake magana da ƴan jaridu a wurin taron Ajaero ya yi allah wadai da tayin biyan  ₦48,000 da gwamnatin tarayya ta yi a matsayin mafi ƙarancin albashi.

Ya ce gwamnatin ba da gaske take ba kan tattaunawa da take da  ƴan kungiyar ƙwadagon.

Ajaero ya ce gwamnati na da kwanaki har zuwa ƙarshen wannan watan domin ta fitar da matsayarta  kan batun.

Tun da farko ƙungiyoyin TUC Da NLC sun miƙawa gwamnati buƙatar ta riƙa biyan ₦615,500 a matsayin mafi ƙarancin albashi.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...