Ƙungiyar ƙwadago ta ƙi amincewa da ₦48,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi

Taron zaman ganawa da ƴan kungiyar ƙwadago da gwamnatin ta tarayya ta kira  ya tashi babu shiri bayan da wakilan kungiyar ƙwadago suka fice daga taron.

Gwamnatin ta kira taron ne domin tattaunawa kan batun mafi ƙarancin albashi da za a riƙa biyan ma’aikata a Najeriya.

Joe Ajaero shugaban ƙungiyar ƙwadago ta NLC da kuma Tommy Okon mataimakin shugaban ƙungiyar ƙwadago ta TUC sune suka wakilci ma’aikata a wurin taron.

Da yake magana da ƴan jaridu a wurin taron Ajaero ya yi allah wadai da tayin biyan  ₦48,000 da gwamnatin tarayya ta yi a matsayin mafi ƙarancin albashi.

Ya ce gwamnatin ba da gaske take ba kan tattaunawa da take da  ƴan kungiyar ƙwadagon.

Ajaero ya ce gwamnati na da kwanaki har zuwa ƙarshen wannan watan domin ta fitar da matsayarta  kan batun.

Tun da farko ƙungiyoyin TUC Da NLC sun miƙawa gwamnati buƙatar ta riƙa biyan ₦615,500 a matsayin mafi ƙarancin albashi.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...