Nasiru Abdullahi, wanda aka fi sani da Chile Maidoki, wanda yana daya daga cikin manyan mutane uku da ke cikin jerin sunayen ‘yan sandan jihar Kano da ake nema ruwa a jallo, ya mika kansa ga kwamishinan ‘yan sanda, Mohammed Usaini Gumel.
Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya bayar da rahoton cewa, Chile Maidoki, dan Layin Falwaya Kurna, na daga cikin manyan mutane uku da kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mista Gumel ya bayyana a gaban kotu da ladar N100,000 kowanne.
Ya miƙa kan nasa ne dai a hedikwatar ‘yan sandan jihar Kano ta Bompai a ranar Asabar.
Mika kai da Chile Maidoki ya yi ya sa adadin tubabbun masu laifi ya kai 100 da kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, Mohammad Gumel ya karba, a cewar wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan Kano, SP Abdullahi Kiyawa, ya kuma bayyanawa manema labarai a ranar Asabar.
“Chile Maidoki ya shaida wa ‘yan sanda cewa ya kan kwana a makabartar da ke cikin birnin Kano don kawai kar jami’an tsaro su gano inda yake.
“Yanzu yana kira ga ‘yan sanda da mutanen jihar da su gafarta masa, ya tuba kuma a shirye yake ya yi aiki da ‘yan sanda domin samar da zaman lafiya da ci gaba a jihar,” a cewar Kiyawa.