Ƙasar Amurika ta fara shirin kwashe sojojinta daga Nijar

Gwamnatin kasar Amurka ta fara shirin janye dakarunta daga jamhuriyar Nijar kamar yadda kafar yaɗa labarai ta CBS ta bada rahoto.

Wani jami’in ma’aikatar wajen Amurka ya faɗawa kafar yaɗa labaran cewa Kurt Campbell mataimakin sakataren harkokin wajen Amurka da kuma Ali Lamine Zeine firaministan ƙasar Nijar sun yi wata ganawa ranar Juma’a a birnin Yamai kan yadda za a shirya ficewar dakarun cikin tsari daga Nijar.

Jami’an biyu sun jaddada muhimmancin dangantaka a tsakanin ƙasashen biyu inda suka amince su cigaba da haɗa kai a fannin da ɓukatar su tazo ɗaya.

Ƙasar ta Amurka ta amince ta rufe sansanin sojanta dake garin Agadez inda anan ne ta girke jiragen yaƙinta marasa matuƙi.

Kusan sojan Amurka 1000 ne ke zaune ƙasar ta Nijar inda suke yaƙi da ƙungiyoyin ƴan ta’adda dake yankin Sahel.

More News

Zanga-zanga: An jibge ƴan sanda 4200 a Abuja

Rundunar ƴan sandan birnin tarayya Abuja ta tura ƴan sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haƙuri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...