Za’a Fara Amfani Da Jiragen Da Basu Amfani Da Matuka Don Dakile Rikicin Manoma Da Makiyaya

[ad_1]

Gwamnatin jihar Osun yanzu haka ta bullo da shirin yin amfani da fasahar zamani inda za a fara aiki da jirage marasa matuka, don gano duk inda masu satar shanu suke. Haka Kuma za a samar da layukan waya da za a rika bugawa kyauta don sanar da hukuma yayin da shanu ke barna a gonaki tare da daukar mataki a hukumance.

Wani masanin tsaro Mallam Kabiru Adamu, ya ce wannan mataki ne mai kyau, amma matsalar ita ce, yadda za ayi amfani da bayanan wannan jirge, kasancewar jihar bata da jami’an tsaro na kanta, ya ce muddin ana son samun nasara to akwai bukatar fadakarwa da kuma wayar da kan dukan bangarorin biyu tun da don su ake yi ta yadda zasu bada hadin kai.

A nasu bangaren kungiyoyin makiyaya da manoma, na maraba lale da wannan mataki wanda suka ce zai taimaka masu. Hounarable Khalil Mohammed Bello, shugaban kungiyar makiyaya ta Kullen Allah’ na kasa,

ya ce, lalle wannan shiri zai taimaka kwarai, kana ya nemi gwamnatoci a

dukkan matakai da suyi koyi da gwamnatin jihar Osun na daukar irin

wannan mataki.

Shima Mallam Musa Labaran Wamba na kungiyar manoma ta Najeriya ya ce tabbas wannan tsari na gwamnatin jihar Osun abin a yaba ne, saboda wannan mataki na iya kawo zaman lafiya.

Saurari rahoton Hassan Maina Kaina

[ad_2]

More News

Atiku ya bayar da tallafin miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri babban birnin...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

Mutanen Sokoto na ta murnar kashe ƙasurgumin ɗanbindigar nan Halilu Buzu

Mazauna yankin Sokoto da kewaye na murnar kashe wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Kachallah Halilu Buzu, da sojojin Najeriya suka yi a farmakin da...