Yaushe Shugaba Buhari zai koma Najeriya?

[ad_1]

Shugaba Buhari

Hakkin mallakar hoto
Facebook/Nigeria Presidency

Image caption

Fadar shugaban kasar ta musanta rahotannin da ke cewa Buhari zai wuce kwana 10 a Landan

Fadar Shugaban Najeriya ta ce sai ranar Asabar shugaban kasar zai koma gida bayan kammala hutun aiki da ya dauka.

Shugaban ya tafi birnin Landan ne domin hutun kwana 10, da ya fara a ranar 3 ga watan Agusta.

A farkon wannan makon ne wasu jaridun kasar suka bayyana cewa shugaban ya dage ranar da zai koma Najeriya, inda zai wuce kwanaki goma kamar yadda aka bayyana tun da farko.

To sai dai fadar shugaban ta musanta rahotannin.

Mai taimakawa shugaban na musamman kan yada labarai Malam Garba Shehu ya shida wa BBC cewa a ranar Asabar shugaban zai koma gida.

Garba Shehu ya ce Buhari zai yi kwanaki goma ne da ake aiki a cikinsu, don haka ba za a lissafa da Asabar da Lahadi da ke cikin makonnin da ya yi hutun ba a lissafi.

A bara dai Shugaba Buhari ya shafe watanni yana hutu a birnin Landan, abin da ya janyo ce-ce-ku-ce a kasar.

Shugaba Buhari mai shekara 76 zai sake tsaya takarar neman shugabancin kasar a zabukan da za a yi a watan Fabrairun badi.

[ad_2]

More News

Ribadu ya koka kan yadda jami’an tsaro suke sayarwa da Æ´an ta’adda bindigogi

Mai bawa shugaban shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce wasu daga jami'an Æ´an sanda da kuma sojoji suna É—aukar bindigogi daga...

Gwamnan Legas Sanwo-Olu ya kara mafi ƙarancin albashi zuwa naira 85,000

Gwamnan Jihar Legas, Babajide Sanwo-Olu, ya bayyana shirin gwamnatinsa na fara biyan sabon mafi karancin albashi na N85,000 ga ma'aikatan jihar.Sanwo-Olu ya bayyana hakan...

Sama da mutane 100 aka tabbatar sun mutu a gobarar hatsarin tankar mai a Jigawa

Rundunar Æ´an sandan jihar Jigawa ta tabbatar da mutuwar mutane 140 a hatsarin gobarar tankar mai da ta faru a garin Majia dake kan...

Sojoji sun kashe É—an Boko Haram a Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya na Birged Ta 21 dake aiki da rundunar Operationa HaÉ—in Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso...