Yau Take Ranar Yaki Da Talauci a Duniya

Miliyon mutane ne aka kiyasta cewa suna fama da talauci a duniya matsalar da ake dangantawa da rashin kudade a hannun jama’a sakamakon rashin aikin yi, ko kuma sana’oin dogaro da kai dalili kenan da MDD ta ware ranar 17 ga watan Oktoba domin tayar da gwamnatoci daga barci.

Koda yake talauci wani abu ne da a can baya ake dangantawa da harakokin tattalin arziki, MDD na ganin girman wannan matsala ya fice inda ake zato lura da yadda rashin mutunta ‘yancin dan adam ke karawa jama’a radadin wannan al’amari.

Jamhuriyar Nijer na daga cikin kasashen da ake sakawa a jerin kasashe masu fama da talauci duk kuwa da cewa Allah ya azurta ta da albarkatun karkashin kasa, saboda haka masana ke gargadi akan wasu mahimman ababen da aka yi imani suna yanke talauci.

Hukumomin jamhuriyar Nijar wadanda tun da jimawa suka hango bukatar bullo da matakan cike gibin da karancin amfanin gona ke haifarwa a karshen damuna, sun yi tanade tanade da dama don bunkasa aiyukan noman rani wanda ta wani bangare ke matsayin babban makamin yaki da taluci.

Wasu alkaluman da kungiyoyin kasa da kasa suka bayar na nuni da cewa daga cikin mutane 4 dake fama da talauci a Nijer 3 dukka mata galibinsu mazauna karkara.

A karkashin taken ranar yaki da talauci ta bana MDD ta yi kiran jama’ su hada kai da mutanen da aka gwadawa wariya domin girka sabuwar duniyar da za a mutunta ‘yanci da mutuncin dan adam a duk inda yake a duniya, abin da ke fayyace sabbin kamannin da talauci ke bijirowa gwamnatoci da kungiyoyin kare hakkin bil adama.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...