“Yan Siyasa Su Rungumi Zaman Lafiya”-Farfessa Galadanci

[ad_1]

Bayan sallar idi,limamin babban masallacin kasa dake Abuja Farfesa Shehu Sa’id Galadanci, ya kira ‘yan siyasa da su yi takatsantsan saboda babban zabe da za’a gudanar shekara mai zuwa.

Farfesa Galadanci ya roki ‘yan siyasa da su yi kokarin ilmantar da magoya bayansu tare da wayar da musu da kai kan neman zaman lafiya ta hanyar kaucewa hatsaniya.

Shi ma ministan babban birnin tarayya Muhammad Musa Bello, ya bayyana ranar sallah a matsayin babbar rana dake da matukar mahimmancin gaske. Ya nemi shugabanni a duk matakai su ji tsoron Allah.

Wadansi mazauna birnin na Abuja suna da ra’ayi mabanbanta gameda irin hali da sallar ta same su a ciki. Yayinda Haji Hafsat Sha’aibu ke yiwa Allah godiya saboda koshin lafiya da mallakar abun yin abun sallar, wani cewa ya yi mutane da yawa na cikin wani irin halin rayuwa, saboda shi kansa layyar hadaka ya yi domin rashin kudi.

Akwai wanda ya yiwa Allah godiya kasancewa ya na da rai amma bai samu ya yi yanka ba sanadiyar fama da rashin kudi.

Yanzu dai mata da yara suna kai da kawowa a wuraren shakatawa a ci gaba da bukukuwan sallar.

A saurari rahoton Hassan Maina Kaina

[ad_2]

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...