Yan sanda sun saka dokar hana fita a Gombe biyo bayan kisan Malam Ibrahim Albani

Wasu da ake zargin yan fashi da makami ne sun kashe wani malamin addinin musulunci, Ibrahim Albani a gidansa dake Gobona a unguwar Tabra a jihar Gombe.

Da yake tabbatar da labarin a ranar Alhamis , mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar Gombe, Mahid Abubakar ya ce yan bindigar sun farma gidan marigayin da misalin karfe 3 na daren ranar Laraba.

Abubakar ya ce malamin ya rasa ransa lokacin da yayi kokarin bude fuskar daya daga cikin maharan hakan yasa ya soke shi da wuka da kuma sarar shi da adda

Wannan ne bayanin da matarsa ta yi wa yan sanda a cewar Abubakar.

Ya kara da cewa kwamishinan yan sandan jihar ya bada umarnin yin cikakken bincike domin kamawa tare da hukunta waÉ—anda suka aikata haka.

Har ila yau kwamishinan ya sanar da dokar hana fita daga 12 na dare zuwa 06 na safe saboda yadda yawan aikata laifuka ya karu a jihar.

More News

Rikici ya É“arke a Abuja inda Æ´an jari bola suka kashe mutane 3

Rahotanni sun ce an kashe mutane uku da suka hada da mata biyu da yaro daya a wata arangama da aka yi tsakanin ‘yan...

Ƴan Fashin daji sun kashe sojoji 4 a Zamfara

Edward Buba daraktan yaÉ—a labarai na ma'aikatar tsaron Najeriya ya ce sojoji huÉ—u Æ´an ta'adda suka kashe ranar Lahadi a wani harin kwanton É“auna...

Sojoji sun kashe Tahir Baga kwamanda a ƙungiyar Boko Haram Tahir Baga

Dakarun  sojan Najeriya na rundunar Operation Haɗin Kai sun samu nasarar kashe, Tahir  Baga wani jigo kuma kwamanda a ƙungiyar Boko Haram a cigaba...

Ƴan sanda sun kama wasu ɓarayin wayar wuta

Jami'an bijilante a jihar Legas sun samu nasarar kama wasu Æ´an uwa biyu dai-dai lokacin da suke sace wayar wata na'urar bada hasken wutar...