‘Yan Jarida a Filato sun yi alkawarin taimakawa ga nasarar zabe

A wani taron da cibiyar Humanitarian Dialogue ta shirya wa wakilan kafafen yada labarai a jihar Filato, gabanin manyan zabubbuka dake karatowa a Najeriya, ‘yan jaridar sun yi alkawarin gudanar da aikinsu bisa kundin tsarin aikin.

Jami’in cibiyar Humanitarian Dialogue, Ibrahim Sale Hassan yace sun shirya taron bitar wa ‘yan jaridan ne ganin yadda suke da muhimmaci wajen gudanar da zabe cikin tsanaki.

Jimi’in dake wayar da kan jama’a a hukumar zabe ta kasa dake jahar Pilato, Osaretin Imahiyereobo yayi amfani da dammar wajen shaida wa wadanda keda katunan zabe fiye da guda daya cewa ba zasu iya kada kuri’a ba.

Taron bitar mai taken gudunmowar ‘yan jarida wajen gudanar da zabe ba tare da tashin hankali ba, ya kuma tattauna kan gudunmuwan sauran masu ruwa da tsaki a harkar zabe zasu bayar wajen yin zabe ba tare da an kashe kowa ko lalata dukiya ba.

More News

NDLEA ta kama wani mai safarar hodar ibilis a filin jirgin sama na Kano

Jami'an hukumar NDLEA dake yaƙi da hana sha da kuma fataucin miyagun kwayoyi sun kama wani mutum mai suna, Okafor  Ifeanyi Anthony mai shekaru...

Magoya bayan jam’iyar PDP sun gudanar da zanga-zanga a jihar Edo

Magoya bayan jam'iyar PDP a jihar Edo sun gudanar da zanga-zanga ranar Lahadi a Benin babban birnin jihar kan yadda ake cigaba da tattara...

Magoya bayan jam’iyar PDP sun gudanar da zanga-zanga a jihar Edo

Magoya bayan jam'iyar PDP a jihar Edo sun gudanar da zanga-zanga ranar Lahadi a Benin babban birnin jihar kan yadda ake cigaba da tattara...

Magoya bayan jam’iyar PDP sun gudanar da zanga-zanga a jihar Edo

Magoya bayan jam'iyar PDP a jihar Edo sun gudanar da zanga-zanga ranar Lahadi a Benin babban birnin jihar kan yadda ake cigaba da tattara...