‘Yan Gudun Hijira Sun Koka Kan Rashin Sabunta Katunan Zabe

[ad_1]

Dubban jama’a ne rikicin Boko Haram ya raba da gidajensu a jihohin Borno, Yobe da Adamawa. haka kuma daruruwan wadanda suka koma garuruwansu yanzu haka sun rasa katunan zaben su.

Wannan na zuwa ne a yayinda hukumar zaben Najeriya ta INEC, ta bada zuwa karshen wannan watan na Agusta a matsayin lokacin dakatar da aikin sabunta katin zaben a kasar. Al’ummomin yankunan sun yi korafi ga hukumar INEC, akan cewa ta yiwa Allah ta dube su da idon rahama wajen samar musu katunan zabe kafin karshen wa’adin.

Mr. Adamu Kamale, dan majalisar wakilai dake wakiltar yankunan Madagali da Michika, ya tabbatar da cewa yanzu haka akwai daruruwan jama’a da basu da katunan zabe, ga kuma lokaci na kurewa, lamarin da ka iya hana su gudanar da zabe.

Hukumar zaben INEC, a ta bakin Barista Kassim Gana Gaidam wanda shine kwamishinan hukumar a jihar Adamawa, ta bada tabbacin cewa za’a cigaba da aikin bada katunan a wadannan wuraren.

Yanzu haka ‘yan siyasa, da kungiyoyi da ma shugabanin addini na cigaba da kiran jama’a akan su fito domin sabunta katinan su.

Suleiman MD Numan, wani matashin dan siyasa ya bayyana katin zaben a matsayin makamin kawo sauyi, ba wai fitina ba.

Ga karin bayani a cikin sauti daga Ibrahim Abdul’aziz.

[ad_2]

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...