Yadda aka kona wani da ransa kan neman aure

Somali police

Wasu ‘yan Somaliya sun fara tara kudi ga iyalan wani mutum da aka kona shi har lahira kan batun auren dan dan’uwansa da mata daga wata kabila daban.

Ahmed Mukhtar Salah dai kawun wannan mai neman auren ne wanda dan kabilar Bantu ne, da ya je ya yi baiko da wata mace ‘yar wata babbar kabila a asirce.

Iyayen yarinyar sun tursasawa Mista Ahmed cewa ya nemo wannan yarinya, bayan da suka farga cewa dan dan’uwan nasa ya gudu da ita.

Wakilin BBC Ibrahim Aden ya ce daga baya dai mahaifin yarinyar ya amince ya sanyawa ma’auratan albarka, amma mahaifiyarta da sauran dangi sun ki yarda su yi hakan.

A makon da ya gabata ne aka caka wa Mista Ahmed wuka aka kuma kona shi da ransa inda ya mutu a Mogadishu, babban birnin kasar.

Tuni dai ‘yan sanda suka kama mahaifiyar yarinyar da kuma wasu mutanen da suke da hannu kan wannan aiki.

Kafofin yada labaran kasar sun ruwaito cewa jama’a da dama sun taru a wajen jana’izar Mista Ahmed da aka yi a ranar Lahadi.

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...