Wata Mata Ta Nemi Kotu Da Ta Raba Aurenta Da Mijinta Domin Yana Takura Mata Da Jima’i

[ad_1]








A ranar Laraba ne kotun dake Iseyin jihar Oyo ta warware auren Baliki Oke da mijinta Arowolo bayan kuka da ta kai cewa yana matsa mata da yawan jima’I.

” Shekarun mu 7 da aure amma kuma abin sai kara gaba yake. Kullum dai aka hadu ayi harka. Ya kan dawo daga office da rana tsaka don ya kwanta dani, bayan haka ya koma wurin aiki, Hakan bai hana shi nema na da dare kullum ne kuma.”

Baliki ta ce mijinta kan lakada mata duka a duk ranar da ta ki amince masa domin shi a ra’ayinsa sai ya kwana da mace sau bakwai a rana sannan yake gamsuwa.

Gogan naka kuwa bai musanta haka ba, Arowolo yace tabas yawan son kwana da mace ya zama masa matsala a rayuwa domin har ya nemi magani kan haka.

Arowolo ya roki kotu da kada ta raba auren su cewa ya yi alkawarin neman taimako akan matsalar da yake fama da shi.

Alkalin kotun Adelodun Raheem ya raba auren Baliki da Arowolo kan cewa Baliki da ‘yan uwan ta sun dage cewa ba za ta ci gaba da auren ba.




[ad_2]

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...