Wata kotu a Abuja ta ci tarar hafsan hafsoshin sojojin Nigeria Naira miliyan 11

[ad_1]

Jaridar Vanguard ta yanar gizo ta jiya Alhamis ta bada rahoton cewa wata kotun tarayyar Nigeria dake Abuja ta ci hafsan hafsoshin sojojin Nigeria Janar Tukur Buratai tarar zunzurutun kudi har Naira miliyan goma sha daya saboda cin zarafin da sojoji suka yiwa wasu matasa 11 a jihar Gombe

Mai shari’a Justice Ijeoma Ojukwu ta ce yadda sojojin Janar Buratai suka kama matasa 11 a Gombe, suka tsare su tun daga ranar 6 ga watan Yulin wannan shekarar, suka ci gaba da gana masu ukuba ba ya cikin tsarin mulki ko dokokin Nigeria.

Jaridar Vanguard ta ce Justice Ijeoma Ojukwu ta ba da umurnin a saki matasan a kuma biya kowannensu diyar Naira miliyan daya.

Maganar ta samo asali ne lokacin da matasan suka samu gawar wani dan uwansu a gonarsu a kauyen Shongom dake jihar Gombe. Sun dauki gawar su kaita gida sai sojoji suka gamu dasu suka kama su. Tun daga lokacin ne, 6 ga watan Yuli suka shiga azabar sojojin kamar yadda jaridar Vanguard ta rubuta

[ad_2]

More News

Atiku ya bayar da tallafin miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri babban birnin...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

Mutanen Sokoto na ta murnar kashe ƙasurgumin ɗanbindigar nan Halilu Buzu

Mazauna yankin Sokoto da kewaye na murnar kashe wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Kachallah Halilu Buzu, da sojojin Najeriya suka yi a farmakin da...