[ad_1]
Wasu yan majalisar dokokin jihar Osun da suka fito daga jam’iyar APC mai mulki sun sauya sheka ya zuwa jam’iyar ADP.
Masu sauya shekar sune: Hon. Debo Akanbi dake wakiltar mazabar Ede North, Hon. Abdullahi Ibrahim dake wakiltar mazabar Iwo da kuma Hon.Tajuddeen Famuyide dake wakiltar mazabar Ilesha West.
Shugaban jam’iyar APC na jihar, Toye Akinola shine ya karbi masu sauya shekar a sakatariyar jam’iyar dake jihar.
Akanbi da yakewa yan jam’iyar ta APC jawabi ya ce” munsan tushen jam’iyar APC a jihar kuma mun amince da gwamna Aregbesola cewa za muyi shekara 8 a kan mulki ba tare ya zabi mutumin da zai gaje shi ba.
Sauya shekar na zuwa ne makonni biyu gabanin zaben gwamnan jihar da za ayi ranar 22 ga watan Satumba.
[ad_2]