Wani Mutum yana tafiya a kasa daga Lagos zuwa Abuja domin nuna adawarsa ga takarar Shugaba Buhari.

[ad_1]

Jaridar Vanguard ta yanar gizo ta jiya Alhamis ta rubuta rahoton cewa wani mutum mai suna Malam Isa Muhammad Munlaila dan asalin jihar Borno dake adawa da sake tsayawar Shugaba Muhammad Buhari takara ya soma tafiya a kasa daga Lagos zuwa Abuja.

Isa Muhammad Munlaila ya dauki matakin ne a madadin matasan Nigeria da ya ce an yi masu alkawarin ayyuka da zara Buhari ya zama shugaban kasa. Saboda haka suka hada kai suka zabi shugaban, amma kaico, ya ba su kunya. Maimakon kirkiro ayyuka miliyan uku kamar yadda ya yi alkawari cikin shekaru uku abun da aka samu basu wuce 500,000 ba.

Malam Isa Muhammad Munlaila ya ce babu wanda ya zuga shi ko tunzura shi ya dauki matakin da ya dauka. Ya ce yana yi ne ba domin kudi ba, yana da nashi kudin. Kazalika ba ya cikin wata jam’iyyar siyasa. Yana wakiltar matasan Nigeria ne.

[ad_2]

More News

Atiku ya bayar da tallafin miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri babban birnin...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

Mutanen Sokoto na ta murnar kashe ƙasurgumin ɗanbindigar nan Halilu Buzu

Mazauna yankin Sokoto da kewaye na murnar kashe wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Kachallah Halilu Buzu, da sojojin Najeriya suka yi a farmakin da...