[ad_1]
Firaministan Birtaniya, Theresa May ta iso Najeriya.
Da isowarta May ta wuce fadar shugaban kasa inda yake ganawa da shugaban kasa, Muhammad Buhari.
Firaministan ta samu tarba daga shugaban kasa Muhammad Buhari tare da wasu daga cikin ministocinsa.
Ziyarar May zuwa Najeriya wani ɓangare ne na ziyarar da take wasu ƙasashen Afirka uku.Ta ziyarci kasar Afirka ta Kudu a jiya Talata kana ta wuce kasar Kenya daga Najeriya.
Ya yin da take Najeriya May za ta tattauna da shugaban kasa Muhammad Buhari kan matsalar tsaro da ta addabi kasar, tattalin arziki da kuma kulla yarjejeniyar kan tsaro da kuma tattalin arziki.
Da take magana a birni Cape Town na kasar Afirka ta kudu May ta bayyana Æ´an Najeriya miliyan 87 ne ke rayuwa cikin talauci.
[ad_2]