Ta leƙo ta koma wa Tottenham a hannun West Ham

West Ham celebrate

Tottenham ta ga ta leko ta koma a karawar da ta yi a gida da West Ham United a gasar Premier League karawar mako na biyar ranar Lahadi.

Tottenhma ce ta fara cin kwallo uku tun kan hutu ta hannun Heung-min Son da ya ci a mintin farko daga take leda.

Harry Kane ne ya ci na biyu a minti takwas ana wasa ya kuma kara na uku na kuma biyu da ya ci a fafatawar minti takwas tsakani.

West ham ta fara farke kwallo ne ta hannun Fabian Balbuena, sannan Davinson Sanchez ya ci gida wato Tottenham daga nan West ham ta kara samun kwarin gwiwa saura minti biyar a tashi karawar.

Gareth Bale ya shiga wasan daga baya kuma a karon farko da ya koma Tottenham don buga wasannin aro daga Real Madrid, ya kuma samu damar cin kwallo amma ya barar.

Kadan ya rage Kane ya ci ta uku rigis a wasan, bayan da ya buga kwallo ya bugi turke, daga nan kuma Tottenham ta rage sa kaimi karawar tana cin 3-2.

Daf da za a tashi ne West Ham ta yi bugun tazara kuma kwallo ta je gidan Tottenham daga baya ta nufi wajen Manuel Lanzini, shi kuwa bai ba ta lokaci ba ya buga ta fada raga.

Da wannan sakamakon Tottenham tana nan a matakinta na shida ita kuwa West Ham ta yi sama kadan zuwa matsayi na takwas a kan teburin gasar Premier League ta bana.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...