Sojoji sun kama wani hatsabibin barawo mai garkuwa da mutane a jihar Zamfara

[ad_1]








Sojojin Najeriya da suka fito daga Rundunar Sojan Najeriya Shiya ta Daya, sun kashe wasu barayi biyar ciki har da kasurgumin barawon nan da ake kira da Sani Danbuzuwa da ya fito daga jihar Zamfara.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da aka fitar a Kaduna mai dauke da sahannun jami’in hulda hulda da jama’a na shiryar, Kanal Muhammad Dole.

Ya ce soja daya ya mutu lokacin da suka rufafa yan fashin ya zuwa cikin dajin Kwuyambana dake jihar Zamfara ya yin da wasu biyu kuma suka jikkata ya kara da cewa “Wadanda suka jikkata an dauke su ya zuwa asibitin asibitin sojoji sojojin dake Kaduna kuma suna murmurewa.”

“Sojojin sun amsa kiran kai daukin gaggawa akan ana aikata fashi da makami akan hanyar Birnin Gwari zuwa Funtua inda wasu da ake zargin barayin ne sukai musu kwanton bauna.

“Amma sun samu nasarar fin ƙarfin barayin hakan ya sa suka gudu cikin dajin Kwuyambana dake jihar Zamfara.”

Sanarwar ta kara da cewa sojojin ranar 14 ga watan Agusta sun kama wani hatsabibin mai garkuwa da mutane a kauyen Sambuwa mai suna,Yinusa Sulaiman da ya kware wajen tattauna biyan kudin fansa.

Har ila yau sojojin sun samu nasarar gano bindigogi da dama a wurin da aka yi artabun.




[ad_2]

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...