[ad_1]
A cikin jawabin da ya yi jim kadan da dawowar sa daga kasar Birtaniya, shugaban kasa Buhari ya shawarci ‘yan siyasa da su zage damtse wajen samarda romon dimokuradiya ga al’ummar da suka zabe su, sannan su wayarwa mutanen mazabunsu kai akan su mallaki katin zabe domin samun damar zaben dantakarar da ya kwanta mu su a rayi a zabe mai zuwa na 2019.
Wannan kira na Shugaban kasa Buhari ya sha bamban da kiraye kirayen da aka saba ji a bakin manyan ‘yan siyasar kasar nan, sakamakon yadda ya bada shawarar ba tare da ya nuna a zabe shi ba, kawai ya bayyana cewar ‘yan Nijeriya su zabi dan takarar da ya kwanta mu su a rayi ne sabanin yadda wasu yan siyasar ke yi.
[ad_2]