Shin Ganduje Ya Karbi Cinhanci Ko A’a?

Tun bayan da wasu faya-fayen bidiyo su ka bullo masu nuna Gwamnan jahar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, na karbar wasu kudade da aka ce cin hanci ne, jama’ar ciki da wajen jahar su ka shiga takaddama kan sahihancin faya-fayen bidiyon ko akasin haka.

Wasu daga cikin faya-fayen bidiyon na nuna kamar Gwamnan Ganduje na karba da kuma saka makudan kudaden cikin ambulan da kuma aljuhu, bayan ya karbo daga wadanda aka ce wai ‘yan kwangila ne.

Yayin da wasu ke ganin faya-fayen bidiyon sahihai ne, wasu kuma na ganin an yi dabara ce ta fasahar zamani aka hada faya-fayen, wadda jaridar Daily Nigeria ta wallafa.

Tuni dai gwamnatin Kano, ta bakin Kwanishinan Yada Labarun jahar, Mohammed Garba, ta ce za ta ruga kotu a bi kadi a shari’ance.

A halin da aka ciki kuma, a cewar wakilinmu, “Majalisar Dokoki ta jihar Kano ta kafa kwamitin bincike game da wannan batu mai wakilai 7, wanda zai mika rahotansa ga zauren majalisar cikin makonni hudu masu zuwa.”

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...