Shehu Sani, sanata mai wakiltar mazabar Kaduna ta tsakiya ya ce fitarsa daga jam’iyar APC ba alama ce dake nuna cewa ya daina siyasa ba.
Sani ya fice daga jam’iyar ta APC biyo bayan tirka-tirkar da ta biyo bayan zaben fidda gwani na jam’iyar APC.
Shugabancin jam’iyar na kasa ya yiwa sanata Shehu Sani alkawarin tikitin takara ba tare da hamayya ba amma kuma daga bisani jam’iyar ta mikawa hukumar zabe ta kasa sunan,Uba Sani mai taimakawa gwamna Nasiru El-rufa’i El-rufa’i kan harkokin siyasa a matsayin wanda zai yi mata takara a mazabar Kaduna ta tsakiya.
Hakan ya jawo ficewarsa daga jam’iyar ta APC.
A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter dan majalisar dattawan ya ci alwashin tsayawa zabe a shekarar 2019 inda ya yi alkawarin bayyana sabuwar jam’iyyar sa cikin kwanaki biyu
.