Mataimakin Babban Limamin Masallacin Yobe da Cibiyar Musulunci, Malam Mohammad Ali Goni Kamsulum, ya yi kira ga masu hannu da shuni da su rika raba nama don taimakawa marasa galihu a jihar, musamman a wannan lokaci da tsadar rayuwa ta yi yawa.
Mallam Kamsulum ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake gabatar da hudubarsa a ranar Lahadin da ta gabata yayin Sallar Eid-el-Kabir ta bana a cibiyar Musulunci ta Damaturu.
Mal Ali Goni ya kuma yi kira ga al’ummar musulmi da su so junansu kuma su kasance masu kishin ‘yan’uwansu.
Malamin addinin Musuluncin ya kuma shawarci al’ummar Musulmi da su yi koyi da rayuwar Manzon Allah SAW ta hanyar zaman lafiya da juna da raba nama ga sauran jama’a.