Shehin Musulunci ya nemi masu kuɗi da su raba wa talakawa naman Salla

Mataimakin Babban Limamin Masallacin Yobe da Cibiyar Musulunci, Malam Mohammad Ali Goni Kamsulum, ya yi kira ga masu hannu da shuni da su rika raba nama don taimakawa marasa galihu a jihar, musamman a wannan lokaci da tsadar rayuwa ta yi yawa.

Mallam Kamsulum ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake gabatar da hudubarsa a ranar Lahadin da ta gabata yayin Sallar Eid-el-Kabir ta bana a cibiyar Musulunci ta Damaturu.

Mal Ali Goni ya kuma yi kira ga al’ummar musulmi da su so junansu kuma su kasance masu kishin ‘yan’uwansu.

Malamin addinin Musuluncin ya kuma shawarci al’ummar Musulmi da su yi koyi da rayuwar Manzon Allah SAW ta hanyar zaman lafiya da juna da raba nama ga sauran jama’a.

More News

Wasu matasa uku da ake zargi da garkuwa da mutum sun gurfana a gaban kotu a Kano

Wasu matasa guda uku sun bayyana a gaban wata kotun majistire dake zamanta a unguwar Gyadi-Gyadi dake Kano inda ake tuhumarsu da zargin  yin...

EFCC ta kama tsohon gwamnan Taraba Darius Ishaku

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa ta kama Darius Ishaku tsohon gwamnan jihar Taraba kan zargin al-mundahanar kuɗaɗen...

Kotu ta tsare matashi kan zargin lalata da yarinya ƴar shekara 13

Kotun majistare ta Badagry da ke Legas a ranar Alhamis, ta bayar da umarnin tsare wani matashi dan shekara 28, Stanley Amos, da ake...

Kotu ta ɗaure waɗanda suka yi fashi a bankin Offa da ke jihar Kwara a 2018

Mai shari’a Haleemah Salman ta babbar kotun jihar Kwara da ke zamanta a Ilorin a jiya ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga...