Saudi Arabia Ta Tabbatar Da Mutuwar Kashoogi

Wata sanarwa da ofishin babban lauyan gwamnatin Saudi Arabia ya fitar, da telbijin kasar ta sanar da safiyar yau Asabar, sanarwar na cewa tuni an kama ‘yan kasar Saudi Arabia 18 nasaba da mutuwar Kashoogi kana an kori mai baiwa kotun masarautar Sauiya shawara, Saud al-Qahtani da kuma mataimakin shugaban hukumar tattara bayanan sirrin kasar Ahmed Assiri.

Babban lauyan gwamnatin yace ana nan ana ci gaba da bincike a kan mutuwar Kashoogi

Kamfanin dillancin labaran kasar ya kuma ce Sarki Salman ya bada umarnin kafa kwamitin ministoci karkashin jagorancin yarima Mohammed domin sake kafa hukumar tattara bayanan sirrin kasar.

Kalaman na yau Asabar sune na karon farko da gwamnatin Saudiya ta tabbatar da mutuwar Kashoogi.

A baya Turkiya ta fada cewa an kashe Kashoogi a ofishin jakadancin Saudiya a Istanbul a ranar biyu ga watan Oktoba, amma Saudia Arabia tayi ta musantawa wannan zargi..

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...