Rundunar Sojan Saman Najeriya Ta Kashe Abu Asad Jigo A Ƙungiyar Boko Haram

Bangaren sojan sama na rundunar Operation Hadin Kai ya sanar da kisan Abu Asad ɗaya daga cikin jagororin ƙungiyar Boko Haram.

Ƙarin ƴan ta’ada da dama aka bada rahoton sun mutu a harin da jiragen yaki suka kai musu a maboyar su dake Tagoshe a tsaunukan Mandara.

Edward Gabkwet daraktan yaɗa labarai na Rundunar Sojan Saman Najeriya shi ne ya bayyana haka a wata sanarwa ranar Asabar a Abuja.

Gabkwet ya ce an kai farmakin ne a ranar Juma’a inda ya ce harin na daga cikin mafi nasara da bangaren sojan sama na rundunar Operation Hadin Kai ya kai a ƴan kwanakin nan.

Ya ce kafin kai harin sojojin saman sun ga ƴan ta’adda kusan sama da ɗari tare da wasu motocin yaƙi huɗu suna ta tattaunawa suna raha a tsakanin su a wurin dake da wasu gine-gine uku.

“Biyo bayan kai harin biyu daga cikin ginin sun rushe tare da dukkanin motocin yaƙin da aka lalata su”

“Akwai alamu dake nuna cewa Abu Asad wanda ƙusa ne a Boko Haram bangaren Ali Ngulde da kuma sauran yan ta’ada kamar su Ibrahim Nakeeb, Mujaheed Dimtu, Mustafa Munzir da sauransu na daga cikin ƴan ta’adda da dama da aka kashe a harin.” a cewar sanarwar.

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya ƙirƙiri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a ƙara wa ƴan bautar ƙasa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...