[ad_1]
Rundunar sojin Najeriya ta bayyana cewa sojojin da suka yi zanga-zanga a filin jirgin saman Maiduguri dake jihar Borno za su fuskanci ladabtarwa dai-dai da dokar aikin soja.
Makonni biyu da suka wuce wasu sojoji sunyi bore a filin jirgin saman bayan da suka yi zargin cewa ana shirin tura su bakin daga a yakin da ake da Boko Haram.
Da yake magana ya yin wani taro a Borno, A.M Dikko kwamandan rundunar samar da tsaro ta Operation Lafiya Dole, ya ce boren soja laifi ne dake jawo hukunci.
“Bama hukunci a soja , muna ladabtarwa ne, ladabi shine kashin bayan aikin idan babu ladabi to babu rundunar soja,”ya ce.
“Idan soja ya yi kuskure to dole a gyara masa.”
Dikko ya tunatar da sojojin da suka yi boren kan rantsuwar da suka yi lokacin da ake daukarsu aiki inda ya karfafa cewa dukkaninsu sun shiga aikin ne a kashin kansu.
[ad_2]