Rikicin Kaduna Ya Yi Sanadiyar Mutuwar Mutane 55

Tashin hankalin na ranar Alhamis ya barke ne biyo bayan wata jayayya tsakanin matasan Kristan da na Musulmi a wata kasuwa a jihar Kaduna dake tsakiyar arewacin Najeriya, a cewar mazauna yankin suna fadawa manema labarai.

A cikin wata sanarwa daga ofishin shugaban kasa, mai magana da yawun shugaba Muhammadu Buhari, yace shugaban ya yi Allah wadai da wannan tashin hankali na kasuwar Magani a Kaduna wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane hamsin da biyar.

Kwamishinan ‘yan sandan Kaduna Ahmad Abdur-Rahaman ya fada a ranar Juma’a cewa, an kama mutane 22 da suke da hannu a cikin wannan tashin hankali.

Jami’an jihar Kaduna sun fadawa kamfanin dillancin Faransa cewa an kafa dokar hana fita a kowane lokaci a yankin Kasuwar Magani inda aka yi tashin hankalin.

 

More News

Kwankwaso ya bada tallafin miliyan ₦50 ga mutanen da ambaliyar Borno ta shafa

Tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran jam'iyar NNPP, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya bada tallafin naira miliyan 50 ga mutanen da ambaliyar ruwa a...

Sakamakon NECOn 2024 ya fito

Hukumar shirya jarabawar ta kasa ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare ta watan Yuni/Yuli 2024, inda kashi 60.55 cikin 100 na waÉ—anda suka...

Ƴan Najeriya na shan baƙar wahala—Janar Abdulsalami

Tsohon shugaban kasa, Janar Abdulsalami Abubakar, ya ce wahalhalun da ake fama da su a Najeriya na kara tabarbarewa, kuma rabon kayan agajin ba...

EFCC ta musalta cewa Yahaya Bello na tsare a ofishin hukumar

Hukumar EFCC dake yaƙi da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa ta'annati ta ce tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello baya ya tsare a hannunta. A...