Ƴansanda a jihar Kaduna sun tabbatar da mutuwar mutum guda tare da kama mutane 32 dake da hannu a rikicin da yafaru yan kwanakin nan.
An ruwaito cewa wasu daga cikin mutanen da aka kama sun yi kokarin kona wuraren ibada a unguwanni Hayin Banki da Kawo ya yin da aka kashe mutum guda a Kasuwar Magani aka kuma kama wani dauke da makami.
A wani bangaren kuma gwamnatin jihar ta sassauta dokar hana fita da aka saka a Kachia mai magana da yawun gwamnan jihar Samuel Aruwan shine ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar ranar Asabar.
Aruwan ya ce mazauna Kachia za su iya fita tun daga safiya har ya zuwa karfe biyar na yamma.
Ya kara da cewa mutanen dake aiki na musamman ne kadai aka amince su fita a lokacin da dokar hana fitar take aiki inda ya ce duk wanda ya fita za a kama shi a hukunta.