Ranar Talata za a yi babbar sallah a Najeriya

[ad_1]

Ganin wata

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Babban kwamitin ganin wata a Najeriya ya fitar da wata sanarwa da ke cewa ranar Talata 21 ga wannan watan ne ranar babbar Sallah a Najeriya.

Kwamitin ya fitar da sanarwar ne a shafinsa na Twitter, inda ya bayyana dalilinsa na yin haka:

“A kan batun cewa Saudiyya ta bayyana ranar Dhl Hijjah da ta bambanta da wanda muka riga muka bayyana, kwamitin ganin wata ya tuntubi babban kwamitin Fatawa na kasa a shekarun baya, kuma an fitar da wata Fatawa mai cewa ya kamata mu rika bin hukuncin ganin watan da kasar Saudiyya ta yanke na Dhul Hijjah saboda muhimmancin hawan Arafat.”

Wannan sanarwar ta ci karo da sanarwar farko da kwamitin ya fitar.

Sanarwar kwamitin ta cigaba da cewa, “A kan haka ne Mai Alfarma Sarkin Musulmi, bayan ya tuntubi kwamitin Fatawa da kwamitin ganin wata da sauran malaman addini har da sarakunan gargajiya, ya bayyana Lahadi 12 ga watan Agusta 2018 a matsayin 1 ga watan Dhul Hijjah 1439H.”

A sanadiyyar wannan sauyin, mutane da dama sun fito suna maganganu na nuna rashin gamsuwa da matakin da kwamitin ya dauka.

A shafin kwamitin na Twitter, wasu sun soki wanann mataki:

Hamma @HAHayatu ya bayyana rashin jin dadinsa, “Kamata yayi ku amince cewa bamu fara azumin bana a kan lokaci ba, kuma kwanaki tsakanin Eid el Fitir da Eid al Adha ba sa wuce 70, kuma ba sa kasa 67. Mutane da dama sun ga watan a wurare masu yawa, amma kuka ki amincewa da haka.”

Shi ma Osama Ibraheem @GmIBRAHEEM cewa yayi, “Dama mun san haka za kuyi tun bayan ganin wata Zhul Qada, watan Shawwal bai cika kwana 30 ba, kuma kun yi ta gardama da mu a cikn wannan zauren. Ku koma ku duba, zaku tabbatar da abin da nake cewa.”

Amma wani mutumin mai suna Simwal @Simwal ya bayyana cewa ba Najeriya ce kawai ta sauya ranar babbar sallah ba.

Ya saka wata sanarwa daga mahukuntan Oman da ke bayyana haka:

“Daular Oman ta sauya ranar 29 ga watan Dhul Qadah ta koma 1 ga watan Dhul Hijjah a hukumance saboda sanarwar da Saudiyya ta fitar.”

A nasu bangaren kwamitin ganin watan ya kare kansa daga dukkan zargin da ake ke yi masa.

“Allah zai tambayemu dukkan abubuwan da muka aikata. Masu cewa an ga wata amma mun ki amincewa da bayanansu, kamata yayi su gabatar mana da hujjojinsu – a shirye muke da mu duba. Idan aka hada kwana 30 na Shawwal da 28 na Dhul Qadah da kuma kwana 10 na Dhul Hijjah sun kasance kwana 68 kenan.”



[ad_2]

More News

Mai magana da yawun Tinubu ya ajiye aikinsa na wani lokaci

Mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wani lokaci domin tunkarar matsalar lafiya.Mista Ngelale...

Ali Jita ya koma jam’iyar APC daga NNPP

Mataimakin shugaban majalisar dattawa dattawa, Sanata Barau Jibrin ya karɓi fitaccen mawakin Kannywood, Aliyu Isa Jita daga jam'iyar NNPP ya zuwa jam'iyar APC. Ali Jita...

An yi jana’izar mutumin da ya Æ™irÆ™iri tutar Najeriya

Iyalan marigayi, Pa Taiwo Akinkumi mutumin da ya ƙirƙiro tutar Najeriya sun yi bikin binne shi bayan da gwamnatin tarayya ta gaza cika alƙawarin...

‘Za a Æ™ara wa Æ´an bautar Æ™asa na NYSC alawus’

Babban daraktan hukumar yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) Birgediya Janar Yushau Ahmed, ya tabbatar wa ‘yan bautar kasar cewa za a kara...