[ad_1]
Kocin tawagar kwallon Najeriya, Super Eagles, Gernot Rohr, ya gayyaci ‘yan wasa 24 don wasan neman shiga gasar kofin Afirka da Najeriya za ta yi da Seychelles.
Cikin jerin ‘yan wasan da aka wallafa a shafin Twitter na hukumar kwallon kafar Najeriya, akwai Odion Ighalo da Ahmed Musa da Henry Onyekuru da Alex Iwobi da Kelechi Ihenacho.
Har ila yau ‘yan wasan gaban da aka gayyata sun hada da Simeone Nwankwo da Samuel Kalu.
‘Yan wasan tsakiyar sun hada da Ogenyi Onazi da John Ogu da Wilfred Ndidi da Oghenekaro Etebo da Joel Obi da kuma Kelechi Nwankali.
Cikin wadanda aka gayyato din kuma har da William Ekong da Leon Balogun da Kenneth Omeruo da Bryan Idowu da Chidozie Awaziem da kuma Ola Aina.
Hakazalika a cikin ‘yan wasan bayan da aka gayyato din akwai haifaffen dan jihar Kaduna, Jamilu Colins, da kuma Semi Ajayi.
Masu tsaron gidan da aka gayyato sun hada da Ikechukwu Ezenwa da Daniel Akpeyi da kuma Francis Uzoho.
[ad_2]