Najeriya ta gayyaci ‘yan wasa 24 domin gasar kofin Afirka

[ad_1]

Ahmed Musa

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

Ahmed Musa da ya koma murza leda a Saudiyya na cikin ‘yan wasan da aka gayyato

Kocin tawagar kwallon Najeriya, Super Eagles, Gernot Rohr, ya gayyaci ‘yan wasa 24 don wasan neman shiga gasar kofin Afirka da Najeriya za ta yi da Seychelles.

Cikin jerin ‘yan wasan da aka wallafa a shafin Twitter na hukumar kwallon kafar Najeriya, akwai Odion Ighalo da Ahmed Musa da Henry Onyekuru da Alex Iwobi da Kelechi Ihenacho.

Har ila yau ‘yan wasan gaban da aka gayyata sun hada da Simeone Nwankwo da Samuel Kalu.

‘Yan wasan tsakiyar sun hada da Ogenyi Onazi da John Ogu da Wilfred Ndidi da Oghenekaro Etebo da Joel Obi da kuma Kelechi Nwankali.

Cikin wadanda aka gayyato din kuma har da William Ekong da Leon Balogun da Kenneth Omeruo da Bryan Idowu da Chidozie Awaziem da kuma Ola Aina.

Hakazalika a cikin ‘yan wasan bayan da aka gayyato din akwai haifaffen dan jihar Kaduna, Jamilu Colins, da kuma Semi Ajayi.

Masu tsaron gidan da aka gayyato sun hada da Ikechukwu Ezenwa da Daniel Akpeyi da kuma Francis Uzoho.

[ad_2]

More News

Atiku ya bayar da tallafin miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya bayar da gudunmawar naira miliyan 100 ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Maiduguri babban birnin...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

An saki Sowore bayan kama shi da aka yi  a filin jirgin saman Lagos

Omoyele Sowore ɗantakarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar AAC a zaɓen 2023 a ranar Litinin ya ce an tsare shi na gajeren lokaci a...

Mutanen Sokoto na ta murnar kashe ƙasurgumin ɗanbindigar nan Halilu Buzu

Mazauna yankin Sokoto da kewaye na murnar kashe wani kasurgumin shugaban ‘yan bindiga, Kachallah Halilu Buzu, da sojojin Najeriya suka yi a farmakin da...